in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sudan da Sudan ta Kudu sun cimma daidaito kan yadda za a warware matsalar man fetur
2012-08-04 16:51:52 cri
Kasashen Sudan da Sudan ta Kudu sun cimma daidaito kan batun raba kudin shiga da ake samu daga wajen sayar da man fetur da sauran batutuwa da dama, za su kuma tattauna lokacin da Sudan ta Kudu za ta maido da sayar da man fetur zuwa kasashen ketare, a cewar mista Thabo Mbeki, shugaban tawagar manyan jami'an kungiyar tarayyar Afirka wato AU mai kula da batun Sudan kuma tsohon shugaban kasar Afirka ta Kudu a ranar Asabar 4 ga wata.

A wannan rana, a Addis Ababa, hedkwatar kasar Habasha, mista Mbeki ya gaya wa kafofin yada labaru cewa, yarjejeniyar da bangarorin 2 suka cimma ta shafi dukkan batutuwan man fetur, ciki har da matsalar kudin da za a kashe kan yin jigilar man fetur, sarrafa shi da yin jigilar shi tsakanin kasashen 2 ba a warware ta ba. Ya kara da cewa, Sudan ta Kudu za ta maido da hakowa da kuma sayar da man fetur zuwa kasashen ketare.

Duk da haka mista Mbeki bai yi wani bayani sosai ba, sa'an nan kuma, kasashen Sudan da Sudan ta Kudu ba su bayyana kome ba kan lamarin.(Tasallah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China