in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi bikin baje koli na Lagos a yankin Lekki
2012-08-04 16:48:50 cri

Ranar Jumma'a 3 ga wata, a yankin Lekki na yin ciniki ba tare da shinge ba, wanda kasashen Sin da Nijeriya suka kafa cikin hadin gwiwa, an bude bikin baje koli na Lagos da kuma taron dandalin tattaunawa kan harkokin zuba jari, inda aka samu mahalarta kimanin dari 5 daga kasashen 2.

Liu Xianfa, karamin jakadan kasar Sin da ke Lagos ya ce, yankin Lekki yana zamanto sabon karfin da zai kara azama kan bunkasuwar tattalin arzikin Nijeriya, haka kuma zai taka rawa wajen inganta dangantakar abokantaka a tsakanin Sin da Nijeriya cikin sauri.

Babatunde Fashola, shugaban jihar Lagos ya ce, yin hadin gwiwa da kasar Sin yana iya kyautata karfin Nijeriya na kawo albarka, da inganta kwarewar masana'antun Nijeriya ta yin takara a kasuwannin duniya. Wannan kuma shi ne muhimmin dalilin da ya sa yankin Lekki ya samu goyon baya daga wajen Nijeriya, wanda kuma ya samu nasara. (Tasallah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China