in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rukuni na 10 na 'yan sandan kiyaye zaman lafiya na kasar Sin sun koma birnin Changsha dake Sin
2012-07-30 21:01:40 cri
A ranar 30 ga wata, rukuni na 10 na 'yan sandan kiyaye zaman lafiya na kasar Sin da aka tura zuwa kasar Liberia sun kammala aikinsu na kiyaye zaman lafiya inda suka koma birnin Changsha dake lardin Hunan na kasar Sin.

A watan Yuli na shekarar bara, 'yan sanda 17 daga ofishin 'yan sanda na lardin Hunan, kwalejin 'yan sanda na lardin, ofisoshin 'yan sanda na biranen Changsha, Zhuzhou, Xiangtan da sauran biranen lardin sun je kasar Liberia don gudanar da aikin kiyaye zaman lafiya. Yawan shekarunsu a takaice ya kai 35. Guda 9 daga cikin 'yan sandan sun yi aiki a Monrovia, babban birnin kasar Liberia, kana guda 8 sun yi aiki a sauran sassan kasar. Bisa labarin da aka bayar, an ce, rukunin 'yan sanda na lardin Hunan shi ne rukuni na 10 da kasar Sin ta tura zuwa kasar Liberia don yin aikin kiyaye zaman lafiya. Yayin da suke gudanar da aikinsu, an yi zaben shugaban kasar Liberia. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China