in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD za ta kebe kudi sama da dala miliyan 20 domin taimakawa 'yan gudun hijira dake kasar Sudan ta Kudu
2012-07-28 16:42:05 cri
A ran 27 ga wata, mataimakiyar babban sakataren MDD dake kula da harkokin jin kai, Valerie Amos ta yi shelar kebe kudi sama da dala miliyan 20 domin taimakawa 'yan gudun hijira dake kasar Sudan ta Kudu.

A wannan rana kuma, ofishin kyautata harkokin jin kai na MDD dake karkashin jagorancin madam Amos ya bayyana cewa, a sakamakon rikice-rikicen da suka abku a jihohin South Kordofan da Blue Nile na kasar Sudan, 'yan gudun hijira da yawa sun sheka cikin kasar Sudan ta Kudu a cikin 'yan kwanakin da suka wuce.

A game da wannan matsala, madam Amos ta furta cewa, mutanen Sudan kimanin dubu 170 sun bar gidajensu a sakamakon rikice-rikice da matsalar karancin abinci. Kuma mutanen da suka gudu zuwa kasar Sudan ta Kudu, bayan zuwansu a kasar, sun shiga cikin wani halin kaka-nika-yi. Mutane da yawa sun mutu a sakamakon kamuwa da cututtuka, dalilin rashin samun kulawa.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, an shelanta kebe wannan kudi daga asusun daidaita matsaloli cikin gaggawa na MDD a wannan rana. An yi kiyasin cewa, 'yan gudun hijira kimanin dubu 65 za su ci gajiyar wannan taimako.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China