in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tawagar Madagascar ta tashi zuwa London don halartar gasar wasannin Olympics
2012-07-25 11:04:05 cri
A ranar Talata ne tawagar kasar Madagascar ta tashi zuwa birnin London na kasar Birtaniya, don halartar gasar wasannin Olympics da za a yi can.

Shugaban kwamitin wasannin Olympics na kasar Siteny Andriasoloniaiko ya fada a yayin taron manema labarai a ranar Talata cewa, a hukumance tawagar kasar ta kunshi mutane 26, ciki har da 'yan wasa 7, masu horas da su, shugabannin tawagar, jami'ai daga kwamitin wasannin Olympics na kasar Madagascar da 'yan jaridu guda 3.

'Yan wasa guda 3 ne kawai suka samu nasarar zuwa gasar ta Olympics daga kasar Madagascar, wato Soloniaina Josiane Patricia a bangaren daga kayan nauyi na Kilogram 72 na mata, Fetra Ratsimiziva a bangaren wasan kokawar Judo na Kilogram 81 na maza, da kuma Nathalia Rakotondramanana a bangaren daga kayan nauyi na mata.

Har ila yau, Madagascar tana da wadanda za su wakilce ta bisa gayyatar musamman da aka yi musu, ciki har da 2 a bangaren ninkaya, wanda Fils Rabetsara Alain Estellah da Ramanantsoa Tsilavina Mamitina za su wakilce ta da kuma wasu a bangaren guje-guje guda 2 wanda Ali Kame da Saholinirina Eliane za su fafata.

Wannan dai shi ne karo na 12 da kasar ta Madagascar ke halartar gasar wasannin Olympics. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China