in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Botswana tana son koyon fasahohin Sin kan kawar da talauci
2012-07-24 11:19:31 cri
Ministan kula da harkokin zaman al'umma dake ofishin shugaban kasar Botswana Mokgweetsi Masisi ya bayyana a ranar 23 ga wata cewa, kasarsa ta shirya koyon fasahohin kasar Sin kan kawar da talauci a nan gaba don fitar da mutane masu fama da talauci a kasar da yawansu ya kai dubu 45 cikin hanzari.

A gun taron manema labaru da aka gudanar a birnin Gaborone dake kasar Botswana a wannan rana, Masisi ya bayyana cewa, a karshen watan Yuni, wani rukunin yaki da talauci dake karkashin jagorancinsa ya kai ziyara kasar Sin da Indiya. Rukunin ya yi bincike kan ayyukan yaki da talauci a kasashen biyu, da kuma yin mu'amala tare da manyan jami'an kasashen biyu masu kula da ayyukan yaki da talauci. Ya ce, ayyuka da nasarorin da gwamnatin kasar Sin ta samu wajen yaki da talauci sun burge shi sosai, kasarsa tana son koyon fasahohin Sin a fanonin yaki da talauci ta hanyar kimiyya da fasaha da kara aiwatar da manufofin gwamnati kan mutane masu fama da talauci da dai sauransu.

Jakadan Sin dake kasar Botswana Liu Huanxing wanda ya halarci taron manema labarun ya bayyana cewa, gwamnatin kasar Sin ta samu nasarori da dama wajen kawar da talauci a shekaru fiye da 10 da suka gabata, amma duk da haka tana fuskantar kalubale a wannan fanni. A halin yanzu, kasar Sin babbar kasa ta biyu ce mai karfi tattalin arziki a duniya, amma bisa ma'aunin talauci na MDD, al'ummar Sin fiye da miliyan 100 suna fama da talauci. Yadda za a rage yawan mutanen da ke fama da talauci yayin da ake raya tattalin arzikin kasar shi ne babban kalubalen da kasar Sin ke fuskanta.(Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China