in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kaddamar da makon kasa na taimakon juna a birnin Cotonou na kasar Benin
2012-07-20 11:09:28 cri
Ministan kasar Benin dake kula da harkokin fadar shugaban kasa, Issifou Kogui N'Douro ya kaddamar a ranar Alhamis a Cotonou da bikin ranar kasa ta taimakon juna karo na biyu, inda aka tattara kudade da kayayyaki domin taimakawa ayyukan jama'a. Bikin makon kasa na taimakon juna na farko an gudanar da shi a shekarar 2010, wanda ya taimaka wajen tattara kimanin kudin Sefa miliyan 23 da aka yi amfani da su wajen biyan kudin aikin tiyata ga yara da mata masu nakasa da suka fito daga iyalai matalauta.

A lokacin bikin kaddamar da aikin, an gabatar da bidiyon mutanen da suka samu wannan taimako domin fadakar al'ummar kasar kan matsalar dake janyo hankali ta nakasassu a kasar Benin. A wannan karo na biyu, kusan kudin Sefa miliyan 107 aka samu daga mutanen kasar. A yayin kaddamar da biki a ranar Alhamis, kusan kudin Sefa miliyan 2 aka tattara nan take. Taimakon da aka samu ya fito musammun ma daga kamfanonin wayar salula, hukumomin kasa da kasa da na gwamnati da kuma kamfanoni masu zaman kansu. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China