in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyoyi biyu na NBA za su ziyarci wasan share fagen gasar NBA na kakar bana a kasar Sin
2012-07-18 17:07:04 cri
Hukumar kula da wasan kwallon kwando ta kasar Amurka wato NBA ta sanar a ranar 16 ga wata a birnin New York cewa, kungiyar Miami Heat da Los Angeles Clippers za su ziyarci kasar Sin don halartar wasan share fagen gasar NBA na kakar bana a kasar Sin.

Za a gudanar da gasanni biyu a tsakanin kungiyoyin biyu a ranar 11 ga watan Oktoba a birnin Beijing da kuma a ranar 14 ga watan Oktoba a birnin Shanghai.

Wannan ne karo na 6 da aka gudanar da wasan share fagen gasar NBA a kasar Sin, kana wannan ne karo na farko da kungiyar da ta zama zakara a gasar karon da ya gabata ta kai ziyara kasar Sin don yin gasa.

Kungiyoyin biyu suna da 'yan wasa da suka kware a duniya da dama. A kungiyar Miami Heat, akwai LeBron James, Dwyane Wade, Chris Bosh da kuma Ray Allen. Kana a kungiyar Los Angeles Clippers, akwai 'yan wasa irinsu Blake Griffin, Chris Paul, Chauncey Billups da kuma Lamar Odom.

Wasan share fagen na gasar NBA a kasar Sin yana daya daga cikin wasannin share fage na gasar NBA da aka gudanar a kasashen waje a shekarar bana. A watan Oktoba na bana, kungiyoyi 8 na NBA za su halarci gasanni 8 a wajen Amurka. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China