in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutune 16 ne suka mutu, 30 kuma suka jikkata sanadiyar hadarin motan da ya faru a kudu maso gabashin Morocco
2012-07-10 10:22:06 cri
Majiyoyin tsaro a kasar Morocco sun bayyana cewa, mutane 16 ne suka halaka yayin da a kalla 30 kuma suka jikkata sanadiyar hadarin motan da ya faru a ranar Litinin a kusa da birnin Essaouira da ke kudu maso gabashin Morocco.

Hadarin ya faru ne a kusa da Essaouira, kimanin kilomita 300 kudu maso gabashin Rabat, babban birnin kasar Morocco, yayin da wata bas da ke zuwa daga birnin yawon bude-ido na Agadir ta kife.

Majiyoyin sun bayyana cewa, wasu daga cikin wadanda hadarin ya rutsa da su 'yan kasashen waje ne.

A wani hadari na daban kuma da ya faru a kasar a ranar Litinin da safe, mutane 10 ne suka rasa rayukansu a kusa da arewacin birnin Nador lokacin da wata bas din ma ta kife.

A cewar ofishin kididdiga na kasar, sama da mutane 4,000 ne suke mutuwa yayin da wasu dubbai suke jikkata a ko wace shekara sanadiyar hadarin mota a Morocco. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China