in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wani Baje kolin 'yancin kai na bunkasa kayayyakin na kasar Benin zai gudana a birnin Cotonou
2012-07-05 10:47:49 cri
Baje kolin 'yancin kai, mai taken 'Littoral 2012 ' dake da manuafar bunkasa kayayyakin da ake kerawa a kasar Benin zai gudana daga ranar 20 ga watan Yuli zuwa 5 ga watan Agusta mai zuwa a filin wasanni na "Stade de l'amitie" dake birnin Cotonou, a wata sanarwar da ministar kamfanoni da kasuwancin kasar Benin ta gabatar a ranar Laraba a Cotonou, madam Madina Sephou.

"Wannan baje koli yana cikin tsare tsaren bukukuwan kasa na cikon shekaru 52 da kasar Benin ta samu 'yancin kai, kuma wata dama ce ta yin musanya taskanin manoma da jama'a, nuna daraja da kuma nuna yabo ga kayayyakin da ake kerawa a kasar Benin, da kuma sanar da wata hanyar bunkasuwa wajen fitar da wadannan kayayyaki zuwa kasashen waje", in ji madam Madina Sephou.

Haka kuma a yayin wannan baje koli za a gudanar da ayyuka daban daban musamman ma tarurukan kara ma juna sani, ranakun kungiyar UEMOA, Togo, ECOWAS da kuma Ghana. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China