in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi tir da allawadai da hare haren ta'adancin a kan coci biyu a kasar Kenya
2012-07-03 10:50:09 cri

Babban sakatare janar na MDD, Ban Ki-moon ya yi tir da allawadai da babbar murya kan hare haren ta'adancin da aka kai wa wasu coci biyu dake birnin Garissa na kasar Kenya, wanda a cikinsu akalla mutane 17 suka mutu.

"Wadannan hare hare da gangan dake shafar wuraren ibada, aikata laifi ne kuma da ya kamata a hukunta", in ji mista Ban a cikin wata sanarwar da kakakinsa ya karanta.

"Babu wata hujjar da za'a bada na kai hare hare kan fararen hula da basu ji, basu gani ba. Mutanen da suka kai wadannan hare hare da ma kuma wasu hare haren ta'adanci na baya baya da aka kai a kasar Kenya ya kamata a sanyasu cikin manyan laifuffuka", in ji wannan sanarwa. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China