in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masanan Sin da kasashen waje sun tattauna kan mu'amala tsakanin kasar Sin da kasashen da ke bin addinin Musulunci
2012-06-28 15:38:18 cri
A ranar 28 ga wata, aka kaddamar da taron kara wa juna sani game da wayewar kai ta kasar Sin da kasashen da ke bin addinin Musulunci a nan birnin Beijing, kuma masana na kasashen Sin, Saudiyya, Turkiyya, Malaysia da sauransu, sun halarci taron, inda za su tattauna kan mu'amala tsakaninsu cikin tarihi.

Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Sin Zhai Jun ya halarci bikin bude taron, inda ya bayyana cewa, wayewar kai ta kasar Sin da ta kasashen da ke bin addinin Musulunci na da daddaden tarihi, kuma sun yi koyi da juna yayin da suke kokarin raya kasa, kuma akwai dangantakar sada zumunci cikin jituwa tsakaninsu, kuma irin dangantakar da ke tsakaninsu ta zama abin misali wajen yin mu'amala tsakanin wayewar kai daban daban a duniya. Yanzu, ana girmama mutane masu bin addinin musulunci sama da miliyan 20 a fannin al'adu da addini da zaman rayuwarsu a kasar Sin, su ma sun ba da babbar gudummawa wajen ingiza zaman lafiya da lumana da wadata tsakanin al'umomi daban daban a kasar Sin.

Sakatare janar na kungiyar hadin gwiwa kan kasashen da ke bin addinin Musulunci ta OIC Ekmeleddin Ihsanoglu ya yi jawabi, inda ya bayyana cewa, Sin ta dade tana mu'amala da kasashen da ke bin addinin Musulunci, kuma bangarorin biyu sun samu ci gaba ta mu'amala tsakaninsu, ya yi imani cewa, dangantakar sada zumunta da ke tsakanin kasar Sin da kungiyar OIC za ta samu bunkasuwa.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China