in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
UNHCR ta yaba wa kasar Zambia da kokarinta ta fuskar sha'anin 'yan gudun hijira
2012-06-24 17:10:25 cri
Kwanan baya, hukumar kula da 'yan gudun hijira ta MDD wato UNHCR ta nuna yabo da godiya ga kasar Zambia game da kokarinta ta fuskar sha'anin 'yan gudun hijira, da kuma goyon bayan da take nunawa ga hukumar.

Madam Joyce, wakiliyar hukumar UNHCR da ke kasar Zambia ta bayyana a yayin wani babban taron da aka shirya don tunawa da ranar 'yan gudun hijira ta duniya a ran 22 ga wata a Lusaka, babban birnin kasar, cewar hukumar ta yi matukar farin ciki da ganin cewa, Zambia tana kokarin cika alkawarin da ta yi wajen daidaita harkokin 'yan gudun hijira, jama'ar Zambia kuma sun ba da babban taimakon kayayyaki ga 'yan gudun hijira 'yan asalin kasashen da ke makwabtaka da ita.

Haka kuma Madam Joyce ta ce, UNHCR za ta inganta hadin gwiwa tare da gwamnatin Zambia domin warware matsalar komawar 'yan gudun hijira fiye da dubu goma da ke zaune a Zambia cikin dogon lokaci ta hanyoyin samun gindin zama a wurin da kuma komawarsu gida bisa son rai.

Bugu da kari, mataimakin ministan harkokin cikin gida na kasar Zambia ya yi furuci a yayin taron, cewar gwamnatin Zambia za ta ci gaba da yin kokari wajen warware matsalar 'yan gudun hijira. Gwamnatin kuma za ta dauki matakai daban daban don tsugunar da su, kuma za ta nuna girmamawa ga zabinsu bisa son rai. Yanzu gwamnatin ta riga ta tsara shirye-shirye uku a wannan fanni, kamarsu komawarsu gida bisa son rai, da samun gindin zama a wurin da suke zaune yanzu, kana da tsugunar da su a sauran wurare.(Kande Gao)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China