in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Birnin Niamey zai kasance hedkwatar al'adun musulumci daga bikin ranar biyar ga watan Yuli
2012-06-19 14:30:05 cri
Babban birnin kasar Nijar, Niamey na shirin karbar daga ranar biyar ga watan Yuli mai zuwa wata babbar haduwa mai taken " Niamey, hedkwatar al'adun musulumci " da kungiyar musulunci, ba da ilimi, fasaha da al'adu (ISESCO) ta shirya, a wani labarin da hukumomin kasar suka bayar a Niamey. Kimanin ministoci 27 daga kasashe mambobin kungiyar ISESCO za su halarci wannan dandalin wanda za a kaddamar da bikin budewa a babban a filin wasanni na Palais des Congres  dake birnin Niamey a karkashin jagorancin shugaban kasar Mahamadou Issoufou kuma a gaban idon babban darektan kungiyar ISESCO.

Dalibai daga makarantun addinin musulunci da ke birnin Niamey za su nuna wasu al'adun musulunci, kuma 'yan wasan fasaha na kasar za su nuna wasanni a yayin bikin bude taron. Hazalika kuma za'a shirya wani dandali game da muhimmin tarihin birnin Niamey. A cewar ministan matasa, al'adu da wasannin motsa jikin kasar Kounou Hassane dake bada bayani, " Niamey, hedkwatar al'adun musulunci " wannan shiri ne dake cikin tsarin manyan biranen al'adun musulumci, dake da manufar karfafa hadin kai tsakanin kasashen musulumci, tare da taimakon kungiyar ISESCO. Zaben birnin Niamey ya biyo bayan taron ministocin al'adu na kasashen musulumci karo na uku da ya gudana a birnin Doha na kasar Qatar daga ranar 29 zuwa 31 ga watan Disamban shekarar 2011. (Mamana Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China