in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a bada muhimmanci kan rikicin bashi dake addabar kasashen Turai a gun taron koli na G20
2012-06-16 17:13:59 cri
Shugaban majalisar kula da harkokin nahiyar Turai, Herman Van Rompuy, da shugaban kwamitin kungiyar EU, Manuel Durao Barroso, sun gabatar da wata wasika a ranar 15 ga wannan wata, inda suka bayyana cewa, za a bada muhimmanci kan rikicin bashi dake addabar kasashen Turai a gun taron koli na G20. Kungiyar EU za ta bayar da ra'ayinta kan yadda za a samu ci gaba tare da tabbatar da daidaituwa a gun taron.

Wasikar ta ce, kungiyar EU za ta sanar da kokarin da ta yi wajen tinkarar rikicin bashi ga kungiyar G20, kana za ta bayyana wa kasashe masu halartar taron, niyyarta wajen tabbatar da cikakken yanki mai amfani da kudin Euro da kuma tsarin kudi. An jaddada a cikin wasikar cewa, ana fatan kasar Girka za ta cika alkawarinta da kuma ci gaba da zama a cikin kungiayar mai amfani da kudin Euro. Haka zalika , za a sa kaimi ga samun ci gaban tattalin arziki bisa tsari bai daya a yankin yayin da ake kiyaye yin amfani da kudi iri daya a yankin.

A cikin wasikar, Van Rompuy da Barroso, sun yi kira ga manyan kasashe masu karfin tattalin arziki na duniya, da su bada taimako wajen daidaita tattalin arzikin duniya, kana sun yi imani da cewa, shirin sa kaimi ga samun babban ci gaba na kungiyar G20 na birnin Los Cabos da za a zartas a gun taron koli na kungiyar G20 a wannan karo, zai bada taimako wajen tabbatar da tsarin kudi, da kyautata shi yadda ya kamata.

Wasikar ta jaddada cewa, za a maida hankali kan yadda za a kara samar da aikin yi, musamman ma ga matasa. A gun taron, an yi maraba da kungiyar G20 domin tana ci gaba da yi lura kan batun samar da aikin yi.

Ban da wannan kuma, kakakin babban sakataren MDD Eduardo Del Buey, ya bayyana a wannan rana cewa, babban sakataren MDD Ban Ki-moon ya riga ya mika wata wasika zuwa ga taron koli na kungiyar G20 da za a gudanar a kasar Mexico.A cikin wasikar ya yi kira ga kasashen duniya da su warware rikicin rashin aikin yi ta hanyoyin zuba jari, manufofi ,da kuma matakan sa kaimi ga samar da aikin yi.(Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China