in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabar kasar Malawi ba za ta halarci taro mai zuwa na kungiyar tarayyar Afrika ba
2012-06-15 10:36:23 cri

Gwamnatin kasar Malawi ta sanar a ranar Alhamis cewa, shugaba Joyce Banda ba za ta halarci taro mai zuwa na kungiyar tarayyar Afrika da zai gudana daga ranar 9 zuwa 16 ga watan Juli a Addis Ababa a kasar Habasha ba.

Mataimakin shugaban kasar Khumbo Kachali, shi ne zai jagoranci tawagar kasar Malawi zuwa taron.

Ya kamata taron ya gudana A Lilongwe, babban birnin kasar ta Malawi ne kamar yadda aka tsara shirin a yayin taron karshe na kungiyar. A ranar 8 ga watan Yuni, gwamnatin kasar Malawi ta sanar da cewa, ba za ta iya shirya gudanar da taron ba, sabili da matsaloli game da shugaban kasar Sudan Omar Hassan al-Bsshir da kotun kasa da kasa ta CPI ta ba da sammacin kama shi.

A ranar Talata, kungiyar tarayyar Afrika ta AU ta tabbatar da cewa, taron zai gudana a Addis Ababa, babban birnin kasar Habasha, ba a Lilongwe ba kamar yadda aka furta a baya.(Abdou Halilou)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China