in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar Tarayyar Afrika ta tabbatar da canja wurin da taro na gaba zai gudana
2012-06-13 13:23:53 cri

Kungiyar Tarayyar kasashen Afrika ta AU a ranar Talata ta tabbatar da wurin da za a gudanar da taron kungiyar na gaba. Taron da ya kamata a gudana a watan Juli a Lilongwe, babban birnin kasar Malawi, zai gudana a Addis Abeba, babban birnin kasar Habasha.

A cikin sanarwar da manema labarai suka samu, kungiyar ta AU ta sanar da cewa, babu wani canji da aka samu a game da ranar gudanar da taron daga 9 zuwa 16 ga watan Juli. Kuma taken taron shi ne bunkasa ciniki a cikin nahiyar Afrika.

A ranar 8 ga watan Yuni, mataimakin shugaban kasar Malawi, Khumbo Kachali ya sanar da cewa, kasar Malawi ba ta amincewa da shugaban kasar Sudan, Omar Hassan al-Bashir da ya shiga taron bisa dalilin kotun kasa da kasa ta CPI ke nemansa.

A ranar Lahadin da ta gabata, a cikin wata hira da kamfanin dillancin labarai na kasar Sin Xinhua, shugaban kwamitin kungiyar ta AU Jean Ping ya sanar da cewa, taron na gaba zai gudana ne a hedkwatar kungiyar a Addis Ababa. Kuma kasar Malawi ta dauki wannan mataki ne sabili da matsin da take samu daga kotun kasa da kasa ta CPI.(Abdou Halilou)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China