in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kaasar Nijar zai kai wata ziyarar aiki ta kwanaki biyu a kasar Guinea
2012-06-08 10:06:10 cri
Bisa kokarin karfafa huldar abokantaka da sada zumunci dake tsakanin kasashen Nijar da Guinea-Conakry, shugaban kasar Nijar Mahamadou Issoufou zai kai wani rangadin sada zumunta da aiki na kwanaki biyu tun daga ranar Asabar a Conakry, babban birnin kasar Guinea, bisa goron gyayyata na takwaransa na Guinea Alpha Conde. In ji wata sanarwar da sashen watsa labaru na fadar shugaban kasar ya fitar.

A yayin wannan ziyara dake cikin tsarin karfafa dankon zumunci tsakanin kasashen biyu, za'a shirya wani gagarumin biki a zauren " Palais du peuple " dake birnin Conakry, inda shugabannin biyu za su gabatar da jawabi ga al'ummar kasar Guinea da kuma 'yan kasar Nijar dake zaune a kasar ta Guinea.

Hakazalika za'a gudanar da shawarwari tsakanin tawagogin kasashen biyu kan muhimman batutuwan da suka fi janyo hankalinsu kamar batun karfafa hulda da abokantaka da za su taimakawa moriyar kasashen biyu. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China