in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mauritius na karbar bakuncin wani taron duniya karo na 6 na Afrika kan aikin bada jini
2012-06-07 14:27:02 cri
Kasar Mauritius na kabar bakuncin wani taron kasa da kasa karo na 6 na jama'ar Afrika kan aikin bada jini tun ranar Talata, wanda ya samu mahalartar wakilai 300 daga bangaren gwamnati da masu zaman kansu na kasashen Afrika, Amurka da kuma Turai.

Makasudin wannan taro na kwanaki hudu shi ne samar da hanyoyin bunkasa tsarin aiki da maganar shiga kungiya ga ma'aikatan kasa dake gudanar da aikin bada jini, likitanci da makamantan haka.

Kungiyoyi masu zaman kansu da masu shirya samar da taimakon bada jini, suna iya kafa wani kawance tare da sauran kungiyoyi a wannan fannin dake cikin wasu kasashe.

Hakazalika, dandalin zai taimaka ga yin musanyar fasahohi da labarai kan batutuwan dake da nasaba da aikin bada jini da tsaron jini. Haka ma za'a tattaunawa kan wasu batutuwan da suka shafi kyautatuwar gidajen likita da kiyaye aikin bada jini, ayyukan da aka yi da kuma wanda za a yi a gaba, wato aikin bada jini a Afrika, da tabbatar da ingancin jini daga mutanen da suka bada.

A cikin jawabinsa na bude taron, ministan kiwon lafiya na kasar Mauritius, Lormus Bundhoo ya tunatar da cewa, koda yake likitanci kan aikin bada jini ya samu sauye sauye ta fuskar kiyayewa da inganci, kulawa da tsaron aikin bada jini ya samu cigaba, amma har wannan fanni na janyo hankali. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China