in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An soma janye dakarun kasar Angola daga Guinea Bissau
2012-06-07 13:34:13 cri
Wata kafar watsa labarai ta kasar Guinea Bissau ta sanar da cewa, an soma janye sojojin kasar Angola guda 600 da suka kai agaji a kasar ta Guinea Bissau. An soma janye sojojin ne a ranar Laraba a karkashin sa idon rundunar wucin gadi ta kungiyar CEDEAO ko kuma ECOWAS.

Tun dai ranar Talata ce, jingin ruwan kasar Angola mai sunan "Lunda Rio Mbridge", ya loda tankokin yaki guda 8, da motocin silke na yaki guda 8, da tankoki daukar mai guda 4, da kuma motocin shiga daji guda 3, kamar yadda kafar watsa labaran ta sanar.

Kakakin gwamnatin kasar Guinea Bissau, Fernando Vaz ya tabbatar da cewa, wannan shiri na janye sojojin kasar Angola, da ke gudana karkashin sa idon sojojin kungiyar ECOWAS ko kuma CEDEAO na tafiya daidai. Har yanzu dai tun da aka fara babu wata matsala da aka fuskanta.

Daga bangaren Kanal Wilson Isaac na tawagar sojin kasar Angola, ya sanar da cewa, janye sojojin na gudana ne tare da dauke kayayyakin sojan.

Sojoji 600 na wannan tawagar sun iso Bissau tun ranar 11 ga watan Maris na shekara ta 2011 bisa yarjejeniyar da aka daddale tsakanin kasashen Guinea Bissau da Angola domin taimakawa kasar Guinea Bissau wajen daidaita lamarin tsaro da kariya.(Abdou Halilou)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China