in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sudan da Sudan ta kudu sun kasa cimma matsaya kan batun tsaro
2012-06-06 20:48:26 cri
Jaridar nan da ke fitowa kowa ce a Khartoum babban birnin kasar Sudan, wato Al-Sudani, ta bada rahoto a ranar Laraba cewa, tawagogin Sudan da Sudan ta kudu a tattaunawar da ake a halin yanzu a Addis Ababa, babban birnin kasar Habasha dangane da batutuwan da sassan biyu ba su warware ba sun kasa cimma matsaya kan batun tsaro.

A cewar rahoton, kasashen biyu sun kasa cimma matsaya kan batun tsaro, yayin da mai shiga tsakani na Afirka ya dage zaman taron don baiwa sassan biyu damar kara tuntubar juna.

Jaridar ta ruwaito Omer Dahab, mai magana da yawun tawagar Sudan, yana mai cewa, tawagar sasantawa ta Sudan ta ki amincewa da shirin da tawagar Sudan ta kudu ta gabatar dangane da dage dokar-ta-bacin da aka sanya kan iyaka tare da dawo da wakilicin diflomasiya tsakanin kasashen biyu.

Dahab ya ce Sudan ta yi na'am da muhimmancin wannan bukata na dage dokar-ta-baci da musayar jakadu tsakanin kasashen biyu, amma wadannan ba su da nasaba da batun tsaro, kuma fita ne daga da'irar kokarin shimfida ginshikan tabbatar da tsaro da zaman lafiya tsakanin kasashen biyu kafin su tattauna sauran batutuwan da ba su warware ba. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China