in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta yi kira ga mambobin kasashen kungiyar SCO su kara zurfafa hadin gwiwar tattalin arziki a wannan shiyya
2012-06-06 17:04:36 cri

An kaddamar da dandalin tattauna kan masana'antu da ciniki na kungiyar tattaunawar hadin kai ta birnin Shanghai SCO bisa jigon "zurfafa hadin kai a wannan shiyya, sabon hanyar ci gaba" a safiyar ran 6 ga wata a nan birnin Beijing. Mataimakin firaministan kasar Sin Wang Qishan ya halarci bikin bude taro, inda ya nuna cewa, bisa burin tinkarar kalubaloli daban-daban, Sin na fatan mambobin kasashen SCO su tabbatar da tsare-tsaren hada kai ta fuskar cinikayya tsakaninsu da sa kaimi ga bunkasuwar tattalin arziki a wannan shiyya.

Wang Qishan ya nuna cewa, yanzu, mambobin kasashe suna tinkarar matsalar hada-hadar kudi yadda ya kamata tare da farfado da tattalin arzikin cikin sauri, wannan ya bada zarafi mai kyau wajen yin hadin kai a wannan shiyya.(Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China