in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi kashedi kan tururuwar 'yan gudun hijira a kudancin Sudan
2012-06-05 14:30:02 cri
Babban jami'in hukumar kulla da 'yan gudu hijira na MDD, Guterres Antonio Guterres, ya yi kashedi a ranar Litinin a game da tururuwa da 'yan gudun hijira ke yi daga yankin Arewa maso Gabas zuwa yankin kudancin kasar Sudan, lamarin da ya ke ganin ya kazamce.

Lamarin jin kai a jihar Blue Nile ta kasar Sudan ya kasance cikin wani mawuyacin hali da ke ci gaba da tabarbarewa, a yayin da mutane kimanin dubu 35 'yan gudun hijira ke isa a yankin na Blue Nile a cikin sati 3 na baya bayan nan. Fadan da ke gudana tsakanin dakarun gwamnatin kasar Sudan da dakarun kungiyar 'yan tawaye ta Arewacin kasar shi ne ya haddasa lamarin.

Tun da farko akwai 'yan gudun hijira dubu 70 da kuma yanzu wadannan sabbin zuwa suka karu a kan su a cikin wannan yanki. Hukumar kula da 'yan gudun hijira ta MDD ta gaggauta yin tsokaci kan wannan tururuwa ta 'yan gudun hijira.

A cewar Mista Guterres, wannan sabon canji ne a cikin yanayi jin kai da ya kasance mawuyaci tun can da farko.Ga shi dai yawan 'yan gudun hijira ya karu da dama, kuma yanayin ya kasance ba shi da kyau kwarai da gaske. Mutane da dama sun ci ganyen itace a kan hanya domin su rayu.(Abdou Halilou)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China