Cikin wani yanayi na bacin rai ne, shugaba Alpha Conde na nuna korafinsa kan mutanen da a cewarsa suke maida kasa baya.
Tare kuma da yin Allah wadai da mutanen da suke amfani da matasa wajen gurfanar da wannan kasa, ana maida ta baya ga tsara a yammacin Afrika maimakon su daga tutar kasar zuwa matsayin farko, ganin yadda kasar Allah ya hore mata da dimbin albarkatu.
Alpha Conde ya bayyana ba tare da rufa rufa ba, cewa "kasar Guinea ta sa kai gaba" a halin yanzu a gaban idon wadanda suka gurfanar da kasar, ya nuna cewa, abun da ba'a yi ba a cikin shekaru 25 ana kokarin yin shi a cikin shekaru biyu kawai. (Maman Ada)