in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhu na MDD ya yaba da janyewar sojojin Sudan da Sudan ta kudu daga Abyei
2012-06-01 10:28:50 cri
A ranar Alhamis ne kwamitin sulhu na MDD ya yi maraba da janyewar sojojin Sudan da Sudan ta kudu daga yankin Abyei da ake takaddama a kai, inda ya karfafawa sassan biyu gwiwar ci gaba da warware dukkan batutuwan da har yanzu ba su dai-daita a kansu ba karkashin kudurorin MDD da suka dace.

Mambobin kwamitin sulhu na MDD mai kasashe 15 sun fada cikin wata sanarwar da suka bayar cewa, sun yi maraba da janyewar sojojin Sudan da Sudan ta kudu daga yankin Abyei, suna masu jaddada cewa, wajibi ne janyewar ta kunshi 'yan sanda da 'yan sandan da ke kula da harkar mai.

Sanarwar ta ce, mambobin kwamitin sulhun sun yi maraba da dawowar sassan biyu kan teburin tattaunawa a ranar 29 ga watan Mayu a Addis Ababa, babban birnin kasar Habasha karkashin kwamitin shiga tsakani na AU.

Kwamitin ya kuma karfafawa sassan biyu gwiwar ci gaba da tattaunawa, ta yadda za su warware dukkan batutuwan da suke korafi a kai karkashin kuduri mai lamba 2046.

Har ila yau, kwamitin ya bayyana damuwarsa kan "rashin samar da kafar kai kayayyakin jin kai a jihohin kudancin Kordofan da Blue Nile. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China