in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An gusa lokacin janyewar sojojin Angola daga kasar Guinea-Bissau
2012-05-31 13:00:38 cri

Janyewar rukunin sojojin wanzar da zaman lafiya da bada taimako ga farfado da bangaren tsaro a kasar Guinee-Bissau (MISSANG), da aka tsaida ranar Laraba, ga dukkan alamu, an gusa wannan lokaci a cewar wata majiya mai tushe ta kusa da rundunar sojojin kasar Guinea-Bissau.

Tawagar MISSANG, dake kunshe da kusan mutane 600, za ta ci gaba da tsayawa har wasu 'yan kwanaki ko ma wasu 'yan makonni in ji wani jami'in rundunar sojojin kasar Guinea-Bissau, da ya bukaci sakaya sunansa. Babu wata ranar da aka tsaida duk da cewa, kungiyar tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika (ECOWAS) ta bayyana a makon da ya gabata cewa, janyewar za ta fara wannan Laraba kuma za ta kwashe tsawon kwanaki hudu ko biyar.

"Jirgin ruwan da zai yi jigilar wadannan sojoji da kuma kayayyakinmu har yanzu bai iso Luwanda ba, domin haka muke jira." in ji wani hafsan sojojin Angola. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China