in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ana kaddamar da taron kolin kasa da kasa na 4 na kamfanonin musulmai a birnin Beijing
2012-05-28 15:26:49 cri
Kungiyar raya ciniki ta kasar Sin da kungiyar sada zumunci tsakanin kasar Sin da kasashen Larabawa suna kaddamar da dandalin koli na hudu na kasa da kasa na kamfanonin musulmai a birnin Beijing daga ran 26 zuwa 29 ga watan Mayu. A ran 27 ga wata, kungiyar addinin musulunci, kungiyar raya cinikin al'ummar kasar Sin da sauran kungiyoyi har ma da 'yan kasuwa da wakilan kamfanonin musulmai na kasar Sin sun halarci bikin kaddamar da dandalin.

A gun bikin bude taron, mataimakin shugaban kungiyar raya cinikin al'ummar kasar Sin Lan Jun ya ce, an kaddamar da bikin ne da zummar sa kaimi ga sana'ar da ta shafi musulmai, kara yin hadin kai tsakanin kasar Sin da sauran kasashen musulmai da habaka hadin kai tsakaninta da sauran kasashe, da kuma samar da wani dandalin tattaunawa kan batun sana'ar da ta shafi musulmai a duniya.

Shugaban kungiyar addinin musulunci na kasar Sin babban liman Chen Guangyuan ya ce, a 'yan shekarun nan, kamfanonin musulmai na samun ci gaba mai kyau wadanda suka taka rawa wajen sa kaimi ga bunkasuwar tattalin arzikin al'umma.

A nan kasar Sin, kabilu fiye da 10 ciki har da Hui, Uighur, Kazak da sauransu mabiya addinin musulunci ne kuma yawansu ya kai miliyan 23.(Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China