in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Mauritaniya ta samu tallafin kudin Euro miliyan 2.5 domin taimakawa matan kasar
2012-05-21 10:34:34 cri
Cibiyar taimakawa cigaba ta kasar Faransa (AFD) ta kebe Euro miliyan 2,5 domin taimakawa wani tsarin cigaban mata a yayin da suke juna biyu a kasar Mauritaniya wato ' rangwame ga mata masu ciki' a cewar wata sanarwa mai tushe.

Wadannan kudade za su taimakawa wajen cigaban wannan tsari da aka jima ana aiwatarwa a kasar Mauritaniya dake taimakawa, a kan kudin Ouguiyas 5000 kwatankwacin dalar Amurka 20 za a iya daukar nauyin gudanar da wasu bincike da bada kulawa ga mata masu juna biyu.

A cewar ministan kiwon lafiya na kasar, dokta Ba Housseinou Hamamdy, wannan taimakon kudi na AFD zai tallafa ga bunkasa da kuma karfafa manufar kasa ta bada rangwame ga mata, da kuma cika gibin taimakon da ya wuce kan tsarin kasa na lafiyar uwa da dan ta, wanda ya taimaka ga tafiyar da aikin a cikin yankuna 6 na cikin kasar.

Tare da samun mutuwar mata 686 wajen haihuwa a cikin haihuwa 100,000 da kuma mutuwar yara 122 a cikin haihuwa 1000, mutuwar uwa da dan ta ta kasance babbar matsala da gwamnatin kasar Mauritaniya ke maida hankali sosai kanta in ji minista Hamamdy. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China