in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kara bunkasa tattalin arziki da samar da karin guraban aikin yi su ne babban nauyin da ke kan G8
2012-05-20 16:19:27 cri
A ranar Asabar 19 ga watan, kungiyar kasashe 8, wato G8 ta bayyana cewa, kara bunkasa tattalin arziki da samar da karin guraban aikin yi su ne mayan nauyi dake kan wuyan kungiyar kasashe 8, wato G8 cikin gaggawa. Ya kamata kasar Giriki ta ci gaba da tsayawa a yankin dake amfani da kudin Euro, kuma kungiyar kasashe 8 za ta dauki dukkan matakan da suka wajaba a kokarin farfado da ci gaban tattalin arziki da kawar da kalubalen da ake fuskanta a kasuwar hada-hadar kudi.

A cikin "Sanarwar Camp David" da kungiyar ta fitar bayan da aka kawo karshen taron koli na kungiyar a ranar 19 ga wata, an nuna cewa, ko da yake an fara samun kyakkyawar alamar farfado da tattalin arzikin kasa da kasa, amma har yanzu ana fuskantar kalubale mai tsanani, saboda haka, an yi maraba da tattaunawar da kasashen Turai suke yi game da yadda za a daidaita manufofin kasafin kudi lokacin da ake kokarin bunkasa tattalin arziki.

Wannan sanarwa ta jaddada cewa, ya kamata kasashen duniya su dauki amintattun matakan farfado da kuma bunkasa tattalin arziki wadanda za su taka rawa wajen kara saurin bunkasa tattalin arziki da biyan bukatun da ake da su ba tare da wata tangarda ba. Amma tabbas ne wadannan matakan tattalin arziki da ya kamata kasashe daban daban su dauka za su sha bamban. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China