in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
PNUD ta taimakawa kasar Nijar da kudin Sefa biliyan 3 domin karfafa zaman lafiya
2012-05-20 16:09:58 cri
Tsarin MDD domin samun cigaba na PNUD ya taimakawa kasar Nijar da dalar Amurka miliyan 6.1 kwatankwacin kudin Sefa biliyan 3 domin ayyukan karfafa zaman lafiya musammun a arewacin kasar ta Nijar. Wannan taimako za'a amfani da shi wajen karfafa karfin babbar hukumar karfafa zaman lafiya da kuma kwamitin kasa na karbar da sa ido kan makaman da suke shiga kasar ta muguwar hanya, wadanda hukumomi guda biyu na kasa sun kasance wasu dabarun karfafa makomar zaman lafiya a kasar Nijar.

Kasar Nijar dai na fama da matsalolin da suke da nasaba da tashe tashen hankali da rikicin siyasa musammun ma na kasashen Mali da Libiya.

A cewar ministan kasar Amadou Boubacar Cisse, gwamnatin Nijar a gaban wadannan matsaloli ta dauki wasu matakan gaggawa da suka shafi daidaita musammun ma munanan sakamako kan tattalin arzikin kasar ta hanyar aiwatar da dabarun tsaro dana cigaba a yankunan Sahara. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China