in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bukaci Afrika da ta kebe kashi 15 cikin 100 na kasafin kudinta kan kiwon lafiya har zuwa shekarar 2015
2012-05-18 10:32:44 cri
Gwamnatocin kasashen nahiyar Afrika ya kamata su kebe kashi 15 cikin 100 bisa na kasafin kudinsu ga kiwon lafiya, in ji wani kwamitin shawara na Afrika na kungiyoyin addinai a ranar Alhamis, 17 ga wata. Babban mai fada a ji, kuma mamba na wannan kwamiti, Boniface Adoyo ya gayawa manema labarai a birnin Nairobi cewa karancin kudin da ake kashewa kan harkokin kiwon lafiyar jama'a ya kasance daya daga cikin matakan dake janyo karin adadin yawan mace macen mata da kananan yara a Afrika.

"Muna kiran gwamnatocin nahiyar Afrika da su girmama sanarwar Abuja ta shekarar 1999 dake bukatar a kalla a ware kashi 15 cikin 100 na kasafin kudin kasashen zuwa harkokin kiwon lafiya," in ji mista Adoyo a yayin wani taron kasa da kasa mai taken "imani domin rayuwa". (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China