in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Afrika ta kudu ta jadada goyon baya ga takarar Uwargida Dlamini Zuma a kwamitin UA
2012-05-16 11:16:04 cri

A ranar Talata, gwamnatin kasar Afrika ta kudu ta sake jaddada kawo goyon bayanta a game da takarar ministar harkokin cikin gida ta kasar, uwargida Dlamini-Zuma, mai neman matsayi mafi girma a kujerar kwamitin kungiyar tarrayar Afrika.

Uwargida Dlamini-Zuma na samun goyon baya daga gwamnatin kasar Afrika ta kudu da kuma kungiyar tattalin arziki da bunkasa kasashen kudancin Afrika ta SADC. Wadanda kuma ke ganin 'yar takarar ta cancanta, kamar yadda Maite Nkoana-Mashabane, ministar hulda da kasa da kasa ta kasar Afrika ta kudu, ta sanar a garin Pretoria.

Uwargida Dlamini -Zuma,'yar takarace da za ta kare darajar nahiyar baki daya , kamar yadda ka'idodin kungiyar tarrayar Afrika suka yi amana a kan matakai na siyasa, da kuma abun da taron manyan jami'ai ya tsayar. Ba wai tana takara ba ne, domin kare darajar wata kasa ba, ko kuma wani yankin ba, cewar Uwargida Nkoane -Mashabane.

Yankunan kudu da na arewaci ba su taba samun sukuni ba na jagorantar kwamitin kungiyar tarrayar Afrika, cewar Ministar.

Ta sanar da cewa, Unwargida Dlamini-Zuma na da bukatar goyon bayan kasashe masu magana da harshen Faransanci a game da wannan zabe. Yankin kuma zai ci gaba da gudanar da tattaunawa da dukkan bangarori na nahiyar a game da takarar Uwargida Dlamini- Zuma, kamar yadda ministar ta jadada. (Abdou Halilou)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China