in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kamfanin Orlean na Nijeriya ya sake ba da kyautar kudi ga wuraren da girgizar kasa ta shafa a Wenchuan
2012-05-11 20:57:24 cri
A ranar Jumma'a 11 ga wata, kamfanin zuba jari na Orlean Invest West AFR da ke Nijeriya ya yi shekaru 5 a jere yana bai wa wuraren da girgizar kasa ta shafa a gundumar Wenchuan ta lardin Sichuan da ke kasar Sin kyautar kudi. A wannan rana, a Abuja, babban birnin Nijeriya, mista Deng Boqing, jakadan kasar Sin a kasar Nijeriya ya gana da malam Sani Mukhtar Kurawa, jami'in kula da harkokin kamfanin na Abuja, inda ya karbi kyautar kudin a madadin gwamnatin kasar Sin.

A yayin ganawar, Sani ya bayyana cewa, ko da yake kamfaninsa na da nisa sosai a tsakaninsa da kasar Sin, amma kullum yana mai da hankali kwarai da gaske kan girgizar kasar da ta faru a Wenchuan. A ko wace shekara ya kan ba da kyautar kudi da yawansa ya kai dalar Amurka dubu 20 ga wuraren da bala'in ya shafa, bisa ga ruhun jin kai. Ya kara da cewa, shekarar bana, shekara ce ta cikon shekaru 4 da abkuwar bala'in. Manyan nasarorin da gwamnatin Sin ta samu wajen farfado da wadannan wurare bayan bala'in sun samu amincewa sosai. Farfado da wadannan wurare na bukatar dogon lokaci, don haka kamfanin zai ci gaba da bayar da kyautar kudi a nan gaba. (Tasallah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China