in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya za ta fara cefanar da ayyukan tauraron dan-Adam dinta ga jama'a
2012-05-11 20:16:41 cri
Wani babban jami'in gwamnati a Najeriya ya fada cewa, sabon tauraron dan Adam din da kasar ta harba mai binciken doron duniya wato Nigeria Sat-2, yanzu an shirya sayarwa jama'a ayyukan da tauraron dan-Adam ke samarwa.

Babban darektan hukumar bincike da ci gaban harkokin sararin samaniya (NASRDA) Mohammed Seidu ne ya bayyana hakan ranar Jumma'a a Abuja. Yana mai cewa, nan ba da dadewa ba za a sauko da tauraron dan Adam na farko na kasar wato Nigera Sat-1.

Seidu wanda ke bayyana ayyukan hukumar, ya ce an kammala gwajin tauraro dan Adan na Sat-2 din da aka harba a watan Agustan shekara ta 2011, kuma nan ba da dadewa ba, za a fara cefanar da ayyukansa ga jama'a.

Najeriya dai ta kasance kasa ta 3 a Afirka da ke da tauroron dan Adam a sararin samaniya baya ga Afirka ta kudu da Algeria a lokacin da ta harba NigeriaSat-1. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China