in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Cadi za ta rika kai man fetur zuwa kasar Afrika ta Tsakiya
2012-05-08 14:22:04 cri
Kasar Cadi za ta fara kai man fetur zuwa kasar Afrika ta Tsakiya, a cewar wata yarjejeniyar da aka sanyawa hannu a ranar Litinin a N'Djamena, babban birnin kasar Cadi, tsakanin Mahamat Kasser Younous, darektan janar kamfanin man fetur na kasar Cadi (SHT) da darektan janar na daidaitawa da sa ido kan farashin man fetur na kasar Afrika ta Tsakiya.

A cewar Leopol Mboli, ministan makamashi da man fetur na Afrika ta Tsakiya, kasashen biyu na shirin sanya hannu kan wasu yarjejeniyoyin kasuwanci a cikin watanni masu zuwa.

"wadannan shawarwari na samun kulawa mai kyau daga manyan jami'an kasashen biyu", in ji Mboli.

A nasa bangaren, ministan makamshi da man fetur na kasar Cadi, Ibrahim Hileou ya ce, "dangantaka a tsakanin kasashen biyu da kuma tsakanin al'ummomin biyu na cikin yanayi mai kyau ta misalin dunkulewa da hadin kai na Afrika."

Shugaban kasar Cadi Deby Itno ya kai wata ziyarar aiki da zumunci a kasar Afrika ta Tsakiya a ranakun Asabar da Lahadi. A cikin wata sanarwar hadin gwiwa, kasashen biyu sun nanata niyyarsu ta karfafa huldar dake tsakaninsu a fannoni da dama musamman ma ta fuskar tsaro, tattalin arziki da kimiyya. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China