in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Masar ta bayyana bakin ciki dangane da zanga-zangar da aka yi wa ofishin jakadancin Saudiyya da ke kasar
2012-04-29 17:32:03 cri
Gwamnatin kasar Masar a ranar 28 ta bayar da sanarwa, inda ta bayyana bakin ciki dangane da yadda aka yi zanga-zanga a ofishin jakadacin kasar Saudiyya da ke kasar, kuma ta sake jaddada muhimmancin huldar da ke tsakanin kasashen biyu.

A labarin da kamfnain dillancin labarai na MENA na kasar Masar ya bayar, an ce, bayan da kasar Saudiyya ta sanar da rufe ofishin jakadancinta a kasar Masar tare da dawo da jakadanta a wannan rana, Mohamed Hussein Tantawi, shugaban kwamitin kolin rundunar sojin kasar Masar ya aika da sako ga sarkin kasar Saudiyya, Abdullah Bin Abdul-Aziz, inda ya yi fatan ganin Saudiyya za ta iya sake yin tunani a game da wannan kuduri, kuma ya sake jaddada irin huldar 'yan uwantaka da ke tsakanin kasar Masar da ta Saudiyya.

Daga ranar 24 zuwa 27 ga wannan wata, daruruwan 'yan kasar Masar sun yi ta yin zanga-zanga a ofishin jakadancin kasar Saudiyya da ke kasar ta Masar, inda suka yi kira ga Saudiyya da ta sako wani lauyan kasar Masar da ta kama. A ranar 28 ga wata, gwamnatin kasar Saudiyya ta sanar da cewa, sakamakon yadda ofishin jakadancinta da ke Masar ke fuskantar barazana daga masu zanga-zangar, ta yanke shawarar rufe ofishin jakadancinta da ke birnin Alkahira da kuma kananan ofisoshin jakadancinta da ke biranen Suez da kuma Alexandria, tare da dawo da jakadanta.(Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China