in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Togo ta shirya bikin murnar cika shekaru 52 da samun 'yancin kai
2012-04-28 16:43:27 cri

A ranar Jumma'a 27 ga wata, Jamhuriyar Togo ta kwashe kusan sa'o'i 3 tana gudanar da wani gagarumin bikin duba faretin soja, har ma sojoji da jama'a sun gudanar da bukukuwa cikin fara'a domin taya murnar cika shekaru 52 da samun 'yancin kai a Lome, babban birnin kasar.

Dubban mutane, ciki har da shguaba Faure Gnassingbe da sauran kusoshin kasar da jakadun kasashen waje da ke kasar da wakilan hukumomin majalisar dinkin duniya dake kasar da wakilan bangarori daban daban na kasar sun halarci bikin. Haka kuma, mawaka da 'yan raye-raye wadanda suka fito daga kasashen Kwadivwa da Burkina Faso da sauran kasashen yammacin Afirka sun halarci bikin bisa gayyatar da aka yi musu.

A ranar 26 ga wata da dare, shugaba Faure Gnassingbe na Togo ya bayar da wani jawabi ga jama'ar kasar, inda ya yi fatan ganin 'yan kasar Togo sun yi kawar da takkadamar da ake samu a tsakanin jam'iyyun siyasa daban daban, ta yadda za su yi kokarin taimakawa wajen zamanintar da kasar Togo domin baiwa 'yan kasar Togo ne damar yiin mulki da kansu. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China