in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumar ikon mallakar ilimi ta kasar Sin za ta yaki da kayan jabu da na marasa inganci
2012-04-26 17:00:52 cri
Yau Alhamis 26 ga wata a nan birnin Beijing, mataimakin shugaban sashin kare ikon mallaka na hukumar ikon mallakar fasaha ta kasar Sin Wu Xiaoming ya ce, hukumar za ta kara karfin yaki da kayan jabu da na marasa inganci da harkokin karya ikon mallakar fasaha. Tare da kafa wani tsarin da ya dace a wannan fanni domin tabbatar da cewa, an gudanar da wannan aiki yadda ya kamata.

Wu Xiaoming ya yi wannan furuci ne yayin da ya halarci wani taro dangane da wannan fanni, inda ya ce, Sin ta gudanar da aikin yaki da kayan jabu da marasa inganci da harkokin karya ikon mallakar fasaha daga watan Oktoba na shekarar 2010 zuwa watan Yuli na shekarar 2011, inda aka samu ci gaba mai kyau. Muhimmin aiki da aka sa gaba shi ne yin kwaskwarima a wasu yankuna da kasuwani da suka fi fama da wannan matsala. Ban da wannan kuma, kara karfi a wannan fanni da tsai da tsarin sa ido wajen kiyaye ikon mallakar fasaha da kyautata dokoki da shari'a a wannan fanni.

Ranar 26 ga wata ya kasance ranar kiyaye ikon mallakar ilim ta kasa da kasa. A wannan rana kuma, hukumar ta kasar Sin ta gabatar da jerin sunayen manyan batutuwa guda 10, manyan matsaloli guda 10 da mutane mafi shahara a wannan fanni guda 10 na shekarar 2011. Ciki har da batun kamfanin Huawei na kasar Sin da ta kai kara a gaban kotu domin zargin karya ikon mallakar fasaha da kamfanin Motorola ya yi, wanda kuma aka samu sulhu tsakaninsu. A ganin wasu masana, abin ya zama abin koyi wajen tabbatar da ikon kamfanonin kasar Sin wadanda suke kasashen ketare.(Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China