in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kamfanonin watsa shirye-shiryen TV na kasashen Sin da Afirka ta Kudu suna gogayya sosai a Najeriya
2012-04-22 19:33:51 cri
A kwanakin baya, wakilin gidan redion kasar Sin da ke Nijeriya, ya yi nazari kan shirye-shiryen talibijin da kamfanoni daban daban suke watsa wa a Nijeriya, inda ya samu labari cewa, kamfanonin kasar Sin da Afirka ta kudu suna yin takara sosaia a tsakaninsu.

Kamfanin kasar Sin da ke watsa shirye-shiryen talibijin a Nijeriya wato kamfanin Startimes, wanda ya shiga cikin kasuwar Nijeriya ba da dadewa ba, ya samu karbuwa matuka, sakamakon shirye-shirye masu inganci, ban sha'awa da kuma araha da ya ke watsawa, musamman ma wasu shirye-shirye cikin harshen Sinanci, domin haka galibin Sinawa da ke Nijeriya suna sha'awar kallon wadannan shirye-shiryen.

Daya daga cikin kamfanonin da ke takara da kamfanin Startimes shi ne DSTV daga kasar Afrika ta kudu. hakika, akwai masu kallon DSTV da yawa a Nijeriya, sannan ya ji tasirin takarar da suke da kamfanin kasar Sin, wannan ya sa ya aiwatar da wasu gyara kan shirye-shiryensa, wato daga wannan shekara da muke ciki, ya fara watsa shirye-shirye cikin harshen Sinanci, domin jawo hankulan masu mu'amula da kamfanin Startimes.(Danladi)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China