in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An soma taron ministocin kiwon lafiya karo na 13 na kungiyar ECOWAS
2012-04-22 19:33:51 cri
A ranar Jumma'ar da ta gabata, a Conakry, babban birnin kasar Guinea, an soma taron ministocin kiwon lafiya na kasashe mambobin kungiyar tarayyar tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika ECOWAS karo na 13. Taron zai diba matsalolin kiwon lafiya a cikin yankin.

Manyan jami'ai masu kula da kiwon lafiya na kasashe guda 15 mambobin kungiyar na halartar taron domin tautaunawa kan maganar kiwon lafiya da ke cikin shirin bunkasuwa na MDGs da MDD ta tsara a shekara ta 2000.

Yankin yammacin Afrika na fuskantar matsalolin kiwon lafiya, kamar rashin sukunin zuwa asibiti da al'umma ke fuskanta sakamakon talaucin da jama'a suke da shi, abun da ya kawo matsalar samun magani yadda ya dace, kuma babu asibitoci masu inganci. Mahalarta taron za su tattauna kan manufar bai daya a cikin yankin ta bangaren kiwon lafiya.

Har wa yau karfafa samar da ma'aikatan kiwon lafiya zai kasance wani abu mai muhimmanci da mahalarta taron za su yi magana a kai.

A yayin da ake gudanar da wannan taro, shugaban kasar Guinea Alpha Conde ya shirya liyafa ga ministocin kasashe mambobin kungiyar ta ECOWAS, inda ya tausaya a game da yanayin da kasashen Afrika suke ciki a bangaren kiwon lafiya. (Abdou Halilou)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China