in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Nijeriya ta rufe wasu kamfanoni guda 2 na lissafi da kididdiga sabili da zamba
2012-04-22 19:33:51 cri
Ma'aikatar kudi ta Nijeriya ta sanar da cewa, gwamnatin kasar ta rufe wasu kamfanoni guda 2 na kididdiga da lissafin kudi na kasar sabili da lamarin zamba a game da sha'anin tallafi a bangaren mai.

Ma'aikatar ta sanar da cewa, an rufe kamfanonin guda 2 da suka hada da kamfanin Akintola-Williams da kamfanin Adekanola bayan da 'yan majalisar wakilan kasar suka gano cewa, kamfanonin na da hannu dumu-dumu a cikin lamarin zamba a kan kudin tallafi ga mai.

A halin yanzu dai gwamnatin kasar ta girka wani kwamiti da zai diba koken da jama'ar da lamarin zambar ya rutsa da su, suna kuma neman samun diyya, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na kasar Sin Xinhua ya samu labari daga ma'aikatar kudi ta kasar Nijeriya.

Majiyoyin da ke da masaniya sun ce, kwamitin zai tabbatar da cewa, mutanen da lamarin zambar ya shafa sun yi koke ne bisa ka'ida.(Abdou Halilou)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China