in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta iya taka muhimmiyar rawa wajen warware batun Syria, in ji jami'in kasar Morocco
2012-04-19 21:13:32 cri
Youssef Amrani, mataimakin ministan harkokin wajen kasar Morocco, wanda ke ziyara a nan kasar Sin, ya furta a Alhamis 19 ga wata cewa, kasar Sin za ta iya taka muhimmiyar rawa mai yakini wajen warware batun Syria.

Mista Amrani ya gaya ma wakilin CRI cewa, kasar Sin , a matsayinta na zaunannen mamban kwamitin sulhu na MDD, za ta iya taka muhummiyar rawa mai yakini kan batun Syria, inda za ta iya sa kaimi ga bangarorin da batun ya shafa da su dakatar da nuna karfin tuwo, da koma wa teburin shawarwari. Ya ce, kasar Morocco da ke da kujerar da ba na dindindin ba a cikin kwamitin sulhun, za ta yi kokari tare da kasar Sin, don samar da nata gudunmawa wajen warware rikicin Syria ta hanyar siyasa. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China