in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Najeriya ta bayyana daukar wasu sabbin matakan bada kariya ga fasinjojin jiragen sama
2012-04-19 11:31:32 cri
Gwamnatin tarayyar Najeriya ta bada wata sanarwa a ranar Laraba cewa, ta bullo da wasu sabbin dokoki da matakai da suka shafi sufurin jiragen sama, da zummar bada kariya ga 'yancin fasinjojin jiragen sama a cikin kasar.

Babban darektan hukumar dake kula zirga-zirgar jiragen saman fararen hula ta NCCA, Harold Demuren ya yi wannan sanarwa a birnin Abuja, inda ya bayyana cewa, sabbin matakan za su taimakawa hukumar yanke hukunci ga duk wani kamfanin jiragen sama na cikin gida ko na waje da zai soke ko kawo jinkiri kan zirga-zirgar jiragen samansa ba tare da wani dalili ba.

Haka kuma za'a sanya allunan bada bayanai na zamani a cikin filayen jiragen saman kasar domin baiwa fasinjoji damar samun karin haske game da tafiye-tafiyensu.

Shugaban NCAA ya nuna cewa, allunan bada bayanai na zamani zasu taimakawa fasinjoji samun kayayyakinsu da suka bace, tare da nuna musu inda kuma zasu iya ajiye kararraki game da wasu matsalolin kamfanonin jiragen saman.

Haka zalika mista Demuren ya bayyana cewa, hukumarsa zata yin hadin gwiwa tare da hukumar tarayya ta filayen jiragen saman kasar Najeriya (FAAN) domin sa ido kan cewa duk filayen jiragen sama suna amfani da wadannan matakai da zasu taimakawa fasinjoji samun 'yancin zuwa kowane filin jiragen saman dake cikin kasar. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China