in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya isa kasar Indiya
2012-03-28 16:53:56 cri
Bisa gayyatar da firaministan kasar Indiya Manmohan Singh ya yi masa, shugaban kasar Sin Hu Jintao ya isa New Delhi, babban birnin kasar Indiya a yammacin Laraba 28 ga wata da yamma don halartar taro karo na 4 na shugabannin kasashen kungiyar BRICS.

Taken taron shi ne "kasashe membobin kungiyar BRICS suna kokarin raya dangantakar abokantaka a fannonin samun zaman lafiya da wadata". A gun taron, Hu Jintao zai bayyana matsayin kasar Sin game da batutuwan kula da harkokin duniya, samun bunkasuwa mai dorewa, hadin gwiwa a tsakanin kasashe membobin kungiyar BRICS da dai sauransu. Bayan taron, za a bayar da sanarwar Delhi.

Yayin da ake gudanar da taron, Hu Jintao zai gana da shugabannin kasashe da abin ya shafa.(Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China