Haka kuma, binciken ya nuna cewa, a shekarar 2011, yawan maza da suka kamu da cutar kanjamau ya kai kashi 2.9 cikin 100, yayin da wannan adadi ya kai kashi 5.6 cikin 100 ga matan kasar. Amma a shekarar 2010, yawan maza da suka kamu da cutar ya kai kashi 4.1 cikin 100, yayin da adadin ya kai kashi 6.8 cikin 100 ga matan kasar.
Ban da wannan kuma, wani jami'in kwamitin yaki da cutar kanjamau na kasar Kamaru ya bayyana cewa, raguwar yawan mutanen da suka kamu da cutar ya dangane da kokari na kasashen duniya da na gwamnatin kasar Kamaru.
A cikin 'yan shekarun nan, Kamaru ta inganta ilmantar da jama'a wajen yaki da cutar kanjamau, kuma sun dauki matakai da dama a game da aikin jinya kyauta ga wadanda suka kamu da cutar.(Bako)