in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin gwamnatin Habasha sun kai farmaki ga dakarun dake kasar Eritrea
2012-03-16 16:51:00 cri

Wani jami'in ma'aikatar watsa labaru ta kasar Habasha ya furta a ran 15 ga wanan wata cewa, sojojin gwamnatin kasar Habasha sun kai farmaki ga dakarun kasar Eritrea a wannan rana.

Ministan gudanarwa na ma'aikatar watsa labaru ta kasar Habasha Shimelis Kemal ya bayyana a gun taron manema labaru da aka yi a yammacin wannan rana da cewa, sojojin gwamnatin kasar sun tsallaka iyakar kasa daga yankin arewa maso gabashin kasar zuwa kasar Eritrea a ranar 15 ga wannan wata da safe. Daga baya sun dakile dakaru a yankuna biyu na kasar Eritrea dake da nisan kilomita 16 zuwa iyakar kasa.

A shekarar 1993, kasar Eritrea ta samu yancin kai ta fita daga cikin kasar Habasha. A watan Mayu na shekarar 1998, kasashen Habasha da Eritrea sun yi musayar wuta mai tsanani a sakamakon neman mallakar yankunan dake iyakarsu. Duk da cewar, kasashen biyu sun kulla yarjejeniyar shimfida tabarmar zaman lafiya a tsakaninsu a shekarar 2000, amma sun ci gaba da samun sabani da yawa a kan batun iyakar kasa. Gwamnatin kasar Habasha ta zargi gwamnatin kasar Eritrea da horar da dakarun dake iyakar kasa domin nuna adawa da gwamnatin kasar Habasha.(Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China