in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za'a bada kyautar farko kan kirkirowa ta nahiyar Afrika a kasar Habasha
2012-03-14 14:28:29 cri
Kwamitin tattalin arziki na majalisar dinkin duniya ta Afrika (CEA), da na kungiyar nahiyar Afrika game da kirkirowa (AIF) sun bada sanarwar kafa lambar kyauta ta kirkirowa a Afrika (IPA) dake darajar kudin Amurka dubu dari ga wanda ya samu matsayi na farko, kana dalar Amurka dubu hamsin ga wanda ya samu matsayi na biyu.

Wannan kyautar za'a gabatar da ita a karon farko a ranar 26 ga watan Maris na shekarar 2012 a Addis Abeba, babban birnin kasar Habasha a gabanin bude zaman taron ministocin kudi na kasashen Afrika da za'a bude a birnin a kalla cikin wannan wata, in ji kungiyar CEA a ranar Talata a cikin wata sanarwa.

A cewar wannan sanarwa, taron zai maida hankali kan ayyukan da suka wajaba domin mayar da Afrika a matsayin wani sabon dandalin bunkasuwa domin cigaban tattalin arzikin duniya. Kuma kyautar ta shekara shekara nada manufar zurfafa ilimi a fannin kimiyya, fasaha da baiwa ga matasa maza da matan Afrika musamman ma bunkasa hanyoyin kirkirowa tare da babbar dama ga harkokin kasuwanci. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China