in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An zabi birnin da za a gudanar da taron wasanni na Afirka na shekarar 2013
2012-03-14 09:20:25 cri
An yi wani taron a kwanakin baya a birnin Bamako na kasar Mali, inda aka zabi birnin da za a gudanar da taron wasanni na Afirka na shekarar 2013, inda birnin Ouagadougo na kasar Burkina Faso ya kasance mai nasarar da zai dauki nauyin gudanar da wanan wasa.

A gun taron, an sanar da wasu 'yan wasa da masu horarwa da su shiga jerin sunayen 'yan wasa mafi shahara a Afirka, ciki har da dan wasan iyo wato nunkaya daga kasar Afirka ta kudu ,mai sunan Penelope Heyns, dan wasan kwallon kafa daga kasar Kongo Francois Mpele, mai bada horo ta fannin fasahar wasan kwallon kafa daga kasar Aljeriya Rabah Saadane, da kuma jami'in kula da wasanni daga kasar Cote- D'Ivoire Lassana Palenfo.

Wakilai fiye da dari daya sun halarci taron, inda suka saurari jawabai game da muhimmiyar rawar da fasahohi suka taka wajen inganta sha'anin wasanni a Afirka.Bugu da kari, memba a kwamitin kula da harkokin wasanin Olympics na kasar Zambia Patrick Chamunda, da takwarorinsa na kasar Poland da Jamus su ma sun halarci taron bisa gayyatar da aka yi musu.

An gudanar da taron bisa kan tallafin da hukumar hadin gwiwa ta wasannin Olympics ta Afirka da kuma kwmaitin kula da wasannin Olympics ta kasar Mali, kana ATP na daya ne daga cikin kafofin watsa labaru da suka bayar da labarai game da wannan taro.(Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China