in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a zabi sabbin 'yan majalisar wakilan jama'ar kasar Sin
2012-03-08 21:36:28 cri

A ranar 8 ga wata, aka mika daftarin kuduri dangane da yawan sabbin 'yan majalisar wakilan jama'ar kasar Sin da za a zaba da kuma yadda za a zabe su ga taron majalisar da a halin yanzu ake yi a nan birnin Beijing, don a yi nazari a kansa. Bisa ga daftarin, a karo na farko ne za a zabi wakilan jama'a bai daya a birane da kuma karkara.

Bisa ga tsarin mulkin kasar Sin da sauran dokokin da abin ya shafa, majalisar wakilan jama'ar kasar Sin ta yanzu za ta cika wa'adin aikinta zuwa watan Maris na shekarar 2013 da ke tafe, kafin lokacin kuma, dole ne a zabi sabbin 'yan majalisar.

A yayin da yake bayani a kan daftarin, Mr.Li Jianguo, mataimakin shugaban zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama'ar kasar Sin kuma babban sakataren majalisar, ya bayyana cewa, abin lura shi ne, wannan karo na farko ne da za a zabi wakilan jama'ar kasar Sin bai daya a birane da kuma karkara, domin kara nuna daidaito tsakanin jama'a da yankuna da kuma kabilu daban daban.

Bisa ga daftarin, za a kara yawan wakilai ma'aikata da manoma da kuma masu fasahohi, musamman ma wakilai manoma. Baya ga haka, za a kuma kara yawan wakilai mata.(Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China