in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin na cimma matsaya daya tare da kasashen makwabta kan batun yaki da ta'addanci, in ji Nuer Baikeli
2012-03-07 16:35:00 cri

Yau Laraba 7 ga wata a nan birnin Beijing, Nuer Baikeli shugaban jihar Xinjiang ta Uygur mai cin gashin kanta, ya nuna cewa, jihar na ciki halin da ya kamata. Bai yarda da duk wani yunkuri da za a yi na kawo barakar kasar Sin ko lalata hadin gwiwar kabilu daban-daban, ko kawo illa ga kwanciyar hankalin al'umma ba. Ya ce, aikin da wasu 'yan ta'adda suka yi, ba zai kawo illa ba ga dangantakar dake tsakanin kasar Sin da ta Pakistan. Sin na cimma matsaya daya tare da kasashen makwabta kan batun yaki da ta'addanci.

An ba da labari cewa, ana kiran taron shekara-shekara na majalisar wakilan jama'ar kasar Sin a nan birnin Beijing, an bude kofa daki, inda wakilan jama'a na jihar Xinjiang suke tattaunawa kan rahoton gwamnatin da firayim ministan kasar Sin Wen Jiabao ya yi kwanan baya, ga manema labaru a wannan rana.

Game da tambayar da manema labaru suka mika masa na cewa, "ko matakin da 'yan ta'adda na ET suka yi zai kawo illa ga dangantakar dake tsakanin kasar Sin da ta Pakistan?" Sai Nuer Baikeli ya ce, ko da yake, an tabbatar da cewa, kungiyar ta'addanci ta ET na da alaka da kungiyoyin ta'addanci na kasashen dake makwabtaka da kasar Sin, amma gwamnatin Pakistan ta ba da sanarwa sau da dama na cewa, ta ki yarda da duk wani harin da aka kaiwa kasar Sin, kuma za ta kiyaye ikon mulki da babbar moriyar kasar Sin.

Ya kara da cewa, Sin na cimma matsaya daya tare da kasashen dake makwabtaka da ita kan batun yaki da ta'addanci. Ya kamata, kasashen daban-daban sun yi hadin kai game da wannan batu.

Nuer Baikeli , ya kara jaddada wajibcin tabbatar da halin da ake ciki a jihar Xinjiang. Ya ce, ya kamata, a gudanar da doka da shari'a ta yadda ya dace a dukkan fannoni. Ba zai yarda da ko wane mutum ya dauki matakin kawo cikas ga aikin gudanar da doka da shari'a ba. Kuma ba zai amince da duk wani mataki da za a dauka ba wajen kawo barakar kasar da tayar da zaune tsaye .(Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China